![]() |
| Mannir H Kabo |
KABO REPORTERS
Friday, July 17, 2026
SHUGABAN RIKO NA KWALEJIN SHARI'A DA ADDININ MUSULINCI TA AMINU KANO (AKCILS) DA AKAFI DANI DA LEGAL, YA NEMI MAJALISSAR DOKOKIN KANO TA AMINCE KWALEJIN TA ZAMA CIKAKKIYAR KWALEJIN ILIMI
Wednesday, July 15, 2026
Kisan uwa da yayan ta a Kano: Matashin da ake zargi ya ce boka ne ya sa shi ya aikata haka
Kisan uwa da yayan ta a Kano: Matashin da ake zargi ya ce boka ne ya sa shi ya aikata haka
Babbar kotun jihar Kano mai lamba ta 11, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Nasiru Saminu, ta ci gaba da sauraron shari'ar Umar Auwalu, Isyaku Yakubu Chobe da Yakubu Dayyabu, waɗanda ake tuhuma da kisan Fatima Abubakar da 'ya'yanta shida a unguwar Dorayi Ciranci da ke Kano.
A zaman kotun da aka yi ranar Laraba, Umar Auwalu mai shekaru 23, yayin kare kansa, ya shaida wa kotu cewa shi kaɗai ne ya aikata kisan matar kawunsa Fatima Abubakar da 'ya'yanta shida a watan Janairun 2026.
Ya ce wani boka kuma mai sayar da maganin gargajiya mai suna Thomas ne ya ba shi wani turare tare da umartarsa da ya ci gaba da aikata irin waɗannan laifuka.
Umar ya kuma bayyana cewa sauran waɗanda ake tuhuma tare da shi, Isyaku Yakubu Chobe da Yakubu Dayyabu, ba su da hannu a kisan. Ya ce ya ambaci sunayensu ne bayan da ya fuskanci azaba a hannun jami'an 'yan sanda bayan kama shi.
A ɓangaren masu gabatar da ƙara, lauyoyin gwamnati ƙarƙashin jagorancin Barista Safiya Yalwati da Barista Zaharaddeen Hamisu Kofar Mata sun gabatar da jami'in binciken 'yansanda, Kofural Aliyu Jamilu, a matsayin shaida. Haka kuma lauyoyin masu kare waɗanda ake tuhuma sun gabatar da shaidunsu a gaban kotu.
Mai Shari'a Nasiru Saminu ya ɗage ci gaba da sauraron shari'ar zuwa ranar 21 ga Yuli, 2026, domin ci gaba da karɓar shaidu da sauraron ɓangarorin shari'ar.
Ana zargin cewa a ranar 17 ga Janairu, 2026, an kashe Fatima Abubakar da 'ya'yanta shida a gidansu da ke Dorayi Ciranci a Kano. Bayan binciken da 'yan sanda suka gudanar, an kama Umar Auwalu tare da wasu mutum biyu bisa zargin hannu a kisan.
Tun da farko an gurfanar da waɗanda ake zargin a Kotun Majistare ta Nomansland kan tuhume-tuhume takwas da suka haɗa da haɗa baki, kisan kai, fashi da makami da kuma fyade. Daga baya, bayan nazarin da Daraktan Hukumar Gurfanar da Masu Laifi (DPP) ya yi, an mayar da shari'ar Babbar Kotu inda aka sake gurfanar da su kan tuhume-tuhume guda tara.
Yayin da Umar Auwalu ya amsa wasu daga cikin zarge-zargen da ake masa, sauran waɗanda ake tuhuma biyu sun musanta aikata dukkan laifukan da ake zarginsu da su.
![]() |
| Daily Nigerian Hausa |
Sunday, July 12, 2026
Jam’iyyar ADC Bangaren Nafiu Bala Ta Kammala Loda Sunayen ’Yan Takararta a Tsarin INEC Domin Zaɓen 2027
Jam’iyyar ADC Bangaren Nafiu Bala Ta Kammala Loda Sunayen ’Yan Takararta a Tsarin INEC Domin Zaɓen 2027
Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) bangaren Hon. Nafiu Bala Gombe ta sanar da cewa ta kammala loda sunayen ’yan takararta na shugaban ƙasa, mataimakin shugaban ƙasa da kuma ’yan takarar Majalisar Dokoki ta Ƙasa a shafin Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) domin babban zaɓen shekarar 2027.
A cikin wata sanarwa da Hon. Nafiu Bala Gombe, wanda ya bayyana kansa a matsayin Shugaban Jam’iyyar na Ƙasa, ya fitar a ranar 12 ga Yuli, 2026, ya ce matakin ya nuna jajircewar bangarensa wajen kare muradun waɗanda suka kafa jam’iyyar da kuma tsofaffin mambobinta, duk da abin da ya kira ƙalubalen da ke barazana ga tsarin dimokuraɗiyya.
Sanarwar ta ƙara da cewa bangaren ADC na ci gaba da tsayawa kan manufarsa ta tsayar da nagartattun, ƙwararru kuma masu kishin jama’a a matsayin ‘yan takara domin samar da shugabanci nagari, inganta kyakkyawan tsarin mulki da kuma dawo da fata ga al’ummar Najeriya.
![]() |
| Kabo Reporters |
Sojoji sunyi nasarar kashe fitaccen shugaban ’yan bindiga, Kachalla Yellow Danbokolo, daya daga cikin manyan abokan hulɗar Bello Turji.
Rahotanni daga jihar Zamfara sun tabbatar da kashe fitaccen shugaban ’yan bindiga, Kachalla Yellow Danbokolo, daya daga cikin manyan abokan hulɗar Bello Turji.
Kachalla Yellow ya mutu ne bayan wani artabu tsakanin jami’an tsaron Zamfara da tawagarsa a yankin Shinkafi.
Kachalla Yellow Danbokolo ya shahara wajen jagorantar hare-hare, sace mutane domin karɓar kuɗin fansa da sauran ayyukan ta’addanci a yankunan Shinkafi, Sabon Birni, Isa, Goronyo da wasu sassan Arewa maso Yamma.
Jaridar ƙasar Iran ta wallafa sunayen Trump da shugabannin Turai a jerin waɗanda ake son ɗaukar fansa a kansu
Jaridar ƙasar Iran ta wallafa sunayen Trump da shugabannin Turai a jerin waɗanda ake son ɗaukar fansa a kansu
Wata jaridar masu ra'ayin mazan jiya a Iran mai suna Hamshahri ta wallafa jerin sunayen wasu fitattun shugabannin duniya da ta ce suna cikin waɗanda za a ɗauki fansa a kansu sakamakon kisan tsohon Jagoran Addini na Iran, Ayatullah Ali Khamenei.
Rahotanni sun ce Ali Khamenei ya rasu ne bayan hare-haren haɗin gwiwa da Amurka da Isra'ila suka kai a ranar 28 ga Fabrairu, wadda ita ce ranar farko ta yaƙin Gabas ta Tsakiya.
Sabon Jagoran Iran, Mojtaba Khamenei, ya sha alwashin ɗaukar fansa, inda a saƙonsa na farko bayan jana'izar mahaifinsa ya ce, "Ɗaukar fansa shi ne muradin al'ummarmu, kuma dole ne a aiwatar da shi."
Ya kuma ce waɗanda sunayensu ke cikin jerin ba za su samu mutuwar lumana ba.
Jaridar Hamshahri, wadda hukumomin birnin Tehran ke bugawa, ta fitar da hotunan shugabannin ƙasashe 13 tare da saƙon Mojtaba Khamenei. Sai dai sabon jagoran bai bayyana sunayen mutanen da Iran ta ce ta sanya a cikin jerin ba, kuma babu wata shaida da ke nuna cewa gwamnatin Iran ta amince da jerin sunayen da jaridar ta wallafa.
Daga cikin waɗanda ke cikin jerin akwai Shugaban Amurka Donald Trump, Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu, Firaministan Birtaniya Keir Starmer, Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio, Sakataren Tsaron Amurka Pete Hegseth, Shugaban Faransa Emmanuel Macron, Firaministar Italiya Giorgia Meloni da kuma shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz.
A lokacin yaƙin, Iran ta zargi wasu ƙasashen Turai da kin yin Allah wadai da hare-haren da aka kai mata, tare da zarginsu da bai wa jiragen sojin Amurka damar amfani da sararin samansu.
Rahotanni sun kuma ce Mojtaba Khamenei bai fito bainar jama'a ba tun kafin fara yaƙin, kuma an ce ya samu raunuka a hare-haren da suka kashe mahaifinsa.
Rahoton Daily Nigerian Hausa
Sanatan Amurka
Sanata a Amurka da ya yi fice wajen goyan bayan ƙasar Israel Lindsey Graham, ya mutu
Sanatan jam'iyyar Republican mai wakiltar jihar South Carolina a Majalisar Dattawan Amurka, Lindsey Graham, ya rasu yana da shekaru 71 bayan gajeruwar rashin lafiya.
A cikin wata sanarwa da ofishinsa ya fitar a shafukan sada zumunta ranar Asabar, an ce Graham ya rasu ne sakamakon wata "gajeruwa kuma ba zato ba tsammani" rashin lafiya, ba tare da bayyana takamaiman abin da ya yi sanadin mutuwarsa ba.
Sanarwar ta ce iyalansa sun nemi jama'a da su ci gaba da yi musu addu'a tare da girmama sirrinsu a wannan lokaci na jimami.
An zabi Graham a matsayin Sanatan Amurka a shekarar 2002, kuma yana wa'adinsa na hudu yayin da yake neman sake tsayawa takara. Kafin haka, ya taba zama dan Majalisar Wakilai ta Amurka tsakanin shekarun 1995 zuwa 2003.
Ko da yake ya taba neman takarar shugaban kasa a karkashin jam'iyyar Republican a shekarar 2016 tare da sukar Donald Trump a farko, daga baya ya zama daya daga cikin manyan abokan siyasar shugaban Amurkan.
Graham ya kasance daya daga cikin masu bai wa Trump shawara kan harkokin ketare, musamman batutuwan da suka shafi Iran da Rasha. Kwana guda kafin rasuwarsa, ya sanar da cimma yarjejeniya da gwamnatin Trump domin ci gaba da kakaba sabbin takunkumi kan Rasha.
A tsawon rayuwarsa ta siyasa, Graham ya shahara da tsauraran matsayinsa kan manufofin ketare. Ya kasance mai goyon bayan daukar matakai masu tsauri kan Iran tare da mara wa gwamnatin Trump baya kan matakan da ta dauka a rikice-rikicen Gabas ta Tsakiya.
Rasuwarsa na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawa kan bukatar kara bayyana gaskiya game da lafiyar 'yan majalisar dokokin Amurka bayan wasu daga cikinsu sun dade suna fama da matsalolin lafiya.
Daily Nigerian Hausa
Friday, January 2, 2026
GWAMNAN JIHAR BAUCHI YA FALLASA ASIRIN MINISTAN ABUJA NYESOM WIKE
GWAMNAN JIHAR BAUCHI YA FALLASA ASIRIN MINISTAN ABUJA NYESOM WIKE
Maigirma Gwamnan jihar mu na Bauchi Senator Bala Abdulkadir Mohammed (Kauran Daular Usmaniyyah) ya fallasa asiri na makircin da Ministan Abuja Nyesom Wike yake kulla masa da jihar Bauchi gaba daya
Maigirma Gwamna yayi wannan fallasa ne a cikin shirin Sunrise Daily na Channels TV dazu da safe, yace akwai wanda yake shirya min makirci, kuma na san shi, shine Ministan Abuja na yanzu Nyesom Wike, ya fada wa duniya cewa zai kunna wuta a jihata na Bauchi
Kauran Daular Usmaniyyah yaci gaba da cewa; na fahimci Wike ne yake bada umarni wa hukuma irin na EFCC wajen batani, yana bawa mutane cin hanci, yana sayar da filayen Abuja yana amfani dasu wajen cimma burinsa, ba sabon abu bane a gareni saboda na taba rike mukamin Ministan Abuja na shekaru 6 na san komai
Gwamnan Bauchi yaci gaba da cewa; yana da hujjoji daga majiyarsa na sirri dake EFCC wanda suka tabbatar masa da cewa Wike ne yake tsara duk abinda yake faruwa da ‘yan adawar siyasa a Nigeria
Kaura yace tsohon Accountant General dinsa na jihar Bauchi yaci amanata, ni na kaishi Kotu da kaina domin a masa hukunci, daga bisani Kotu ta bada belinsa, to a yanzu Wike ne yake aiki dashi a Kotu wajen bada shaida na karya akan mukarrabaina da aka kama
A matsayina na Gwamna wanda na rike manyan mukamai tun daga Sanata har Minista, ina shugaban al'ummah ta ya zai kasance ina daukar nauyin ta'addanci, ana min wannan sharri ne saboda ina cikin manyan 'yan adawa
Zan bi duk matakan da suka dace domin na kare kaina, na rubuta wa Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya takardan korafi, tare da sanar da hukumomin tsaro, kuma zan kai korafina zuwa ga hukumonin Majalisar dinkin duniya, inji Maigirma Gwamna
Sannan Gwamna Bala yace Shugaban Kasa Tinubu yana kewaye da 'yan daba, 'yan damfara wadanda suke son ha||akashi a siyasance irinsu Wike
Muna rokon Allah Ya kare jihar Bauchi daga wadanda suke neman jingina mana ta'addanci, Allah Ya sa mugun nufinsu ya kare a kansu da iyalansu kadai.






